Ƙungiyar ASUU: 'Ba za mu koma koyarwa ba sai gwamnatin Najeriya ta biya mana buƙatunmu'

 Shugaban majalisar dattijai a Nijeriya ya roƙi malaman jami'o'i su janye yajin aikin da suke yi, su koma su buɗe makarantu don ci gaba da karantarwa.

Sanata Ahmed Lawan, ya yi wannan kira ne yayin wani taro da shugabancin ƙungiyar ta ASUU kan batutuwan da suka danganci yarjejeniyar da malaman jami'o'in suka cimma da gwamnatin tarayya.

Tun da farko, Ƙungiyar malaman jami'o'in ta ce ba za ta bi umarnin gwamnati na bude makarantun da suka shafe sama da wata shida a rufe ba.

Farfesa Haruna Musa shi ne shugaban ASUU reshen jami'ar Bayero Kano, kuma a baya-bayan nan ya shaida wa BBC irin buƙatun da ƙungiyar ke son a biya mata kafin komawa bakin aiki.

Farfesan ya ce sun jima suna yarjejeniya da gwamnatin tarayya a kan bukatun da suke son a biya musu, amma kuma shiru.


Post a Comment (0)
Previous Post Next Post